Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

An cika shekara guda da fara yakin kasar Sudan

Informações:

Sinopsis

A farkon wannan makojn ne yakin da ake gwabzawa a Sudan tsakanin sojojin kasar karkashin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kuma dakarun RSF da ke karkashin Mohamed Hamdan Dagalo ke cika shekara guda. Rikicin da aka faro a ranar 14 ga watan Afrilun shekarar 2023, ya yi sanadiyar rasa rayuka da dama da kuma raba miliyoyi da muhallansu, wanda a yanzu MDD ta ce akwai barazanar barkewar yunwa a kasar.Bangarori da dama ne dai suka yi yunkurin warware wannan rikici amma abin yaci tura.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Nasiru Sani.