Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Matsalar garkuwa da mutane na kara kamari a arewacin Najeriya

Informações:

Sinopsis

A Najeriya an shiga wani yanayi na fargaba da kuma tsoro lura da yadda ‘yan bindiga suka tsananta dabi’ar yin garkuwa da mutane masu tarin yawa a lokaci daya musamman ma a yankin arewacin kasar. A cikin makon da ya gabata kawai, sama da mutane 5,00 ne aka yi garkuwa da su, da suka hada mata ‘yan gudun hijira a jihar Borno, da daliban firamire da sakandare a jihar Kaduna, sai kuma almajiran tsagaya a jiyar Sokoto.Abin tamabayar shine, shin me ke faruwa ne musamman ta la’akari da yadda hukumomin tsaro suka gaza bai wa jama’a kariya a sassan kasar?Anya kuwa gwamnati na da wani tsari da za ta iya aiwatarwa don tunkarar wannan matsala?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.